An Nuna Wa Matasa Illar Shan Miyagun Kwayoyi — Leadership Hausa Newspapers

0
207


Uwar gidan gwamnan jihar Katsina Hajiya Hadiza Aminu Bello Masari, ta bayyana cewar iyayen yara matasa maza da mata musamman iyayen da suka san  ‘ya’yansu na shan miyagun kwayoyi a jihar Katsina da ma sauran jihohin Nijeriya baki daya da su tsawata wa ‘ya’yansu game da shan miyagun kwayoyi.

Uwargidan ta yi wannan tsokaci ne a Kwalejin ’yan mata da ke garin Funtuwa. Yayin da take gudanar da jawabinta a wajen taron tsawata wa da nuna wa matasa illar  shan miyagun kwayoyi Hajiya Hadiza, ta ci gaba da cewa, wajibi ne iyayen yara matasa maza da mata su sanya wa ‘ya’yansu ido game da abokan da suke ma’amala da su domin kauce wa lalatattun abokai  wadanda ke shan miyagun kwayoyi. Sannan kuma ta umarci al’ummar jihar Katsina da Nijeriya baki daya da su hada karfi da karfe domin yakar ko kashe wadannan al’amari mai cutar da matasa. Shi dai wannan taron gwamnatin jihar Katsina ta kirkiro shi, domin samun nasarar kashe wannan al’amari na shan miyagun kwayoyi.

Taron…



Read More…..Leadership Newspaper